Zargin sakaci da rayukan marasa lafiya, musamman mata masu ciki a Asibitin Kwararru na Murtala da ke Kano ya karade kafafen sadarwa a ’yan kwanakin nan.
Ana zargin yadda ma’aikatan asibitin ke nuna halin ko-in-kula da rayukan jama’a na sanadiyyar mutuwar mata da jarirari kusan kowace rana.
Shin me ya sa asibitin Murtala ya yi kaurin suna haka a wurin jama’a?
Shirin Daga Laraba ya tattauna masu korafi kan asibitin da kuma masu fafutukan kawo gyara.