Ana samun korafe-korafe game da yaduwar zinace-zinace tsakanin ma’aurata a Najeriya?
Shin me ya faru ma’aurata suka tsunduma ka’in-da-na’in a harkar alfashar da a baya an fi dangantawa da marasa aure marasa kamun kai?
Shirin Daga Laraba na wannan mako ya tsananta bincike da tattaunawa da masu ruwa da tsaki kan wannan batu domin gano inda gizo ke saka, domin fid-da jaki daga duma.