Shin Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?

Daga Laraba

Daga Laraba
Shin Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?
Jun 18, 2025
Idris Daiyab Bature

Hare haren ‘yan ta’adda na kara ta’azzara a yankuna daban daban na fadin kasar nan wanda hakan ke nuni da Karin rashin tsaro da ya dade yana ciwa alumma da ma gwamnati tuwo a kwarya.


Ko a kwana kwanan nan an ga yadda jihar filato tayi ta fama da irin wadannan hare hare da kuma hare haren ramuwar gayya.

Wani kididdiga kungiyar dake tattara bayanan hare haren ta’addanci ta fitar ya nuna cewa Najeriya ta taso daga mataki na 8 zuwa na 6 a batun ta’addanci a duniya.

Kazalika a kwanakin nan wani hari da aka kai a wasu yankunan jihar Binuwe yayi sanadiyyar halakar mutane da dama, wadda hakan ya jawo cece ku ce da ya kai har wasu na kiran mutane su tashi don kare kan su.

Irin wannan kira dai an dade ana yi, sai dai gwamnati na ganin ba daidai ne mutane su kare kan su daga hare haren ‘yan ta’adda ba.


Shirin Daga Laraba na wannan mako zai yi nazari ne kan shin ko kare kai daga hare haren ‘yan ta’adda zai kawo karshen matsalar tsaro da ake fuskanta a Najeriya?