Dabiar daukar doka a hannunsu ta yadda da an kama mai laifi kafin a yi bincike sai kawai a kaddamar da hukunci ta hanyar duka, sara ko sakawa mutum taya a wuya a zuba fetur a cinna wuta na kara karfi a tsakanin mutane a kwana kwanan nan.
Rahotanni na yawan fitowa daga kudu maso yammaci da Arewa maso yammacin Najeriya kan hukuncin gurguzu ko kuma a ce daukar doka a hannu.
Me yasa hakan ke yawan faruwa?
Ina mahukuntan kasar suke da har rai ke neman zama ba a bakin komai ba?