Yadda Rikicin Rasha Da Ukraine Ya Dugunzuma ‘Yan Najeriya

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Rikicin Rasha Da Ukraine Ya Dugunzuma ‘Yan Najeriya
Feb 25, 2022
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

Yakin da ya barke tsakanin Ukraine da Rasha zai shafi kasashen duniya da dama, musamman wadanda su ka dogara da samun kudin shiga ta hanyar fitar da danyen mai.

a daya gefen kuma akwai yiwuwar a samu fantsamar kananan makamai cikin duniya sanadiyyar wannan yaki idan ya yi kamari.

Shirin Najeriya A Yau na tafe da bayanan musabbabin rikicin da kuma hanyoyin da zai shafi sauran sassan duniya.