Haduwar Ranakun Arfa Da Juma'a A Hajjin Bana
Najeriya a Yau
Najeriya a Yau
Haduwar Ranakun Arfa Da Juma'a A Hajjin Bana
Jul 08, 2022
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

Hajjin bana ya zo da falalar haduwar tsayuwar Arfa da ranar Jumma'a. 
Wadannan ranaku ne masu mahimmanci ga Musulmin duniya, 
wadanda ake karfafa yin azumi da addu'o'i a cikinsu.

Za a yi Babbar Sallah a Najeriya cikin tsadar raguna, 
shin anya za a ci nama kuwa a wannan sallar?
Mene ne kuma hukunce-hukuncen layya?

Shirin Najeriya a yau ya tattauna da malamai, 
kuma wakilinmu a Kano ya zagaye kasuwan raguna don gano mana me yasa raguna suke tsada.