Haduwar Ranakun Arfa Da Juma'a A Hajjin Bana

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Haduwar Ranakun Arfa Da Juma'a A Hajjin Bana
Jul 08, 2022
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us Fan Mail

Hajjin bana ya zo da falalar haduwar tsayuwar Arfa da ranar Jumma'a. 
Wadannan ranaku ne masu mahimmanci ga Musulmin duniya, 
wadanda ake karfafa yin azumi da addu'o'i a cikinsu.

Za a yi Babbar Sallah a Najeriya cikin tsadar raguna, 
shin anya za a ci nama kuwa a wannan sallar?
Mene ne kuma hukunce-hukuncen layya?

Shirin Najeriya a yau ya tattauna da malamai, 
kuma wakilinmu a Kano ya zagaye kasuwan raguna don gano mana me yasa raguna suke tsada.