Dalilan Da Suka Sa 'Yan Najeriya Ba Sa Tuhumar Shugabannin Su
Najeriya a Yau
Najeriya a Yau
Dalilan Da Suka Sa 'Yan Najeriya Ba Sa Tuhumar Shugabannin Su
Jul 14, 2022
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

A Kasashen da suka ci gaba, da zarar ba su gamsu da shugabancin da ake masu ba, 
za su mike tsaye don tuhumar shugabannin na su.

Amma ba safai 'yan Najeriya ke yin irin wannan hobbasan ba. Sun iya hadiye ko wacce irin gurbatacciyar gwamnati.

A Najeriya shugabanni suna tafiyar da harkokin mulkin kasa  yadda suka ga dama, ba ruwan su da ko yan kasa na jin dadin abun da suke yi, ko kuma a’a.  

Shirin Najeriya a yau, ya tattauna da 'yan Najeriya, da masu ruwa da tsaki a kan wannan al'amari.