Abin Da Ya Sa Annobar Kwalara Ta Ki Ci Ta Ki Cinyewa A Kano
Najeriya a Yau
Najeriya a Yau
Abin Da Ya Sa Annobar Kwalara Ta Ki Ci Ta Ki Cinyewa A Kano
Jul 21, 2022
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

Ana iya cewa cutar kwalara ta yi kakagida a Jihar Kano da ma wasu sassan Najeriya inda a duk shekara ake samun barkewar cutar, take kuma lakume rayuka.

Ko a kwana-kwanan nan, ma’aikatar lafiya ta jihar ta ce cutar ta kashe mutum biyar daga cikin 189 da suka kamu da ita a kananan hukumomi 20 na jihar a cikin wata shida .

Shin me ya sa ake yawan samun wannan cuta? Wai shin ina jami’an duba-gari suke, wadanda ke zagayawa unguwa-unguwa, gida-gida domin tabbatar da tsaftar muhalli don guje wa yaduwar cututtuka?

Mun tattauna da mazauna jihar Kano da kuma masu ruwa da tsaki a harkar kiwon lafiya.