Yunkurin wasu kungiyoyi na hana Bankin Jaiz sake gina Kasuwar Taminus da ke Jos a Jihar Filato ya bar baya da kura.
Rahotanni sun bayyana cewa kasuwar da ake takaddamar sake ginawa ita ce ginanniyar kasuwa mafi girma a Afirka ta Yamma.
Shin me ya sa kungiyoyin ba sa so a sake gina kasuwar?
Shirinmu na yau ya binciko irin asarar da ake tafkawa a dalilin rashin kasuwar da ma wasu batutuwa.