Yadda Kabilanci Ke Neman Hana Banki Gina Kasuwar Taminus Ta Jos
Najeriya a Yau
More Info
Najeriya a Yau
Yadda Kabilanci Ke Neman Hana Banki Gina Kasuwar Taminus Ta Jos
Aug 29, 2022
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

Yunkurin wasu kungiyoyi na hana Bankin Jaiz sake gina Kasuwar Taminus da ke Jos a Jihar Filato ya bar baya da kura.

Rahotanni sun bayyana cewa kasuwar da ake takaddamar sake ginawa ita ce ginanniyar kasuwa  mafi girma a Afirka ta Yamma.

Shin me ya sa kungiyoyin ba sa so a  sake gina kasuwar?

Shirinmu na yau ya binciko irin asarar da ake tafkawa a dalilin  rashin kasuwar da ma wasu batutuwa.