Irin Asarar Da Cin Ganda Ke Janyo Wa Tattalin Arzikin Najeriya

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Irin Asarar Da Cin Ganda Ke Janyo Wa Tattalin Arzikin Najeriya
Sep 20, 2022
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

Fatar dabbobi da ake gyarawa ana ci da aka fi sani da ganda ko kpomo na daga cikin arzikin da Allah Ya huwace wa Najeriya, domin kuwa bayan ci a matsayin nama ana amfani da fatu da kiraga wurin yin takalma da jaka da sauransu.

Shin kun san irin asarar da masu cin ganda a matsayin nama ke janyo wa Najeriya kuwa?

Saurari cikakken shirin domin sanin yadda za a sarrafa ganda domin samun kudaden shiga baya ga ci a matsayin nama.