Ranar Laraba 28 ga Satumba da muke ciki ’yan takarar zaben 2023 za su fara yawon tallata manufofinsu ga ’yan Najeriya, gabanin babban zaben kasar da za a gudanar a watan Fabrairu da Maris na 2023.
Lura da yadda kafafen sada zumunta suka yi tasiri a zabukan 2009 a Amurka, Rasha da sauran manyan kasashen duniya, kuna ganin yakin neman zabe a kafafen sada zumunta a Najeriya zai yi wani tasiri na a zo a gani?
Ku biyo mu sannu a hankali cikin shirin domin jin ra’ayoyin masana kan wannan batu.