Shin rikicin cikin gida da yakici, yaki cinyewa a Jam’iyar PDP zai bari dan takararta na shugaban kasa, Atiku Abubakar ya kai bantensa a zaben 2023?
Ci gaba da bijire wa shugabancin jam’iyyar da wasu gwamnoninta biyar ke yi a halin yanzu ya sa a fargabar takarar tsohon mataimakin shugaban kasan na neman shiga halin rashin tabbas.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya bi diddigin wannan batu, ya kuma samar da bayanai masu gamsarawa.