Ranar Juma’a 24 ga Maris Babban bankin Najeriya CBN ya fara sakarwa bankunan kasar tsabar kudi, kuma ya umarcesu su yi aiki a ranakun Asabar da Lahadi.
Shin matakin da babban Bankin ya dauka ya yi tasiri?
Ku biyo shirin namu na yau ku ji halin da ake ciki a Najeriya dangane da samun tsabar kudi a sassa daban daban na kasar.