Yadda Kishi Ya Sa Matar Aure Farka Cikin 'Yar Makwabta Da Wuka

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Kishi Ya Sa Matar Aure Farka Cikin 'Yar Makwabta Da Wuka
May 19, 2023
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

In da ranka, ka sha kallo!
Yanzu haka  ‘yan sanda a Jihar Kano suna farautar wata matar kan zargin ta farka cikin wata karamar yarinya ’yar makwabtansu da wata zabgegiyar wuka, bayan da ta dauki yarinyar a hannun iyayenta, da sunan za ta raka ta unguwa.

Ina dalilin wannan danyen aiki da matar ta yi wa wannan karamar yarinya? 

Wakilanmu a Kano sun bin diddigi sun samo cikakken bayani daga bakin mahaifin yarinyar kamar yadda za ku ji a cikin shirin Najeriya A Yau. 

Ku biyo shirin namu na yau ku ji cikakken bayani.