Yadda Kishi Ya Sa Matar Aure Farka Cikin 'Yar Makwabta Da Wuka

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Kishi Ya Sa Matar Aure Farka Cikin 'Yar Makwabta Da Wuka
May 19, 2023
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us Fan Mail

In da ranka, ka sha kallo!
Yanzu haka  ‘yan sanda a Jihar Kano suna farautar wata matar kan zargin ta farka cikin wata karamar yarinya ’yar makwabtansu da wata zabgegiyar wuka, bayan da ta dauki yarinyar a hannun iyayenta, da sunan za ta raka ta unguwa.

Ina dalilin wannan danyen aiki da matar ta yi wa wannan karamar yarinya? 

Wakilanmu a Kano sun bin diddigi sun samo cikakken bayani daga bakin mahaifin yarinyar kamar yadda za ku ji a cikin shirin Najeriya A Yau. 

Ku biyo shirin namu na yau ku ji cikakken bayani.