Bukatun Al'ummomin Jihohin Arewa 4 Ga Sababbin Gwamnoninsu

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Bukatun Al'ummomin Jihohin Arewa 4 Ga Sababbin Gwamnoninsu
May 29, 2023
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

Yau Litinin 29 ga watan Mayu,  za a rantsar da sabon shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu tare da mataimakinsa Kashim Shettima, kuma a yau din ne  suma sababbin gwamnonin jihohi ke yin rantsuwar kama aiki, a cikinsu akwai wadanda aka zaba a karon farko a matsayin Gwamnoni a Arewa kuma a karkashin tutar wata jam’iya ta daban da wadda ta yi mulki a jihohinsu.

Ko wace fata al'ummomin jihohin Arewacin Najeriya 4 ke da ita game da sababbin gwamnonin da suka zaba daga sun yi rantsuwar kama aiki?

Saurari Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci domin jin fata da zaton 'yan Najeriya ga sababbin shugabanninsu.