Abin Da Ya Hana Rikicin Mwaghavul Da Fulani Ƙarewa A Filato
Najeriya a Yau
More Info
Najeriya a Yau
Abin Da Ya Hana Rikicin Mwaghavul Da Fulani Ƙarewa A Filato
Jul 13, 2023
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Jihar Filato dake Arewa ta tsakiyar Najeriya ta yi ƙaurin suna wajen rikice-rikicen ƙabilanci da addini, domin dai ba kasafai ake shafe dogon lokaci ba tare da an sanya dokar ta ɓaci ba.

Yawancin rikicin ya fi ƙamari tsakanin Fulani makiyaya da kuma manoma. To amma, wa ke da alhaki akan rura wutar wadannan rikice-rikice, kuma ta ina za a lalubo bakin zaren?

Shirin Najeriya a Yau ya yi nazari akan yadda zaman doya da manja ya ƙi ci ya ƙi cinyewa tsakanin ƙabilar Fulani Makiyaya da al’ummar Mwaghavul a jihar Filato.