Rufe iyakar Najeriya da Nijar ya sa al'ummar dake rayuwa a waɗannan yankuna shiga wani hali na tsadar rayuwa, da tsayawar lamura cak.
Masu sana’o’i a iyakokin dake maƙwabtaka da Nijar sun ce rayuwa tana neman tagayyara. Frashin kayan masarufi na daya daga cikin abin da ya fi tada hankali.
Shirin Najeriya a Yau ya leƙa wasu iyakokin Najeriya da Nijar domin ganin yadda rayuwa ta sauya.