Hukumar kula da Harkokin Kasashen Waje Ta Najeriya ta aikewa Hukumar Bada Agajin Gaggawa NEMA sakon Kasar Kamaru na niyyar bude madatsar ruwan Lagdo, sakamakon cikar da madatsar ya yi.
A bara bude wannan madatsa ya raba 'yan Najeriya sama da Miliyan guda da matsugunansu, ko ta wadanne bangarori wannan ruwa zai shafi Najeriya bana?
Shirin Najeriya A Yau na tafe da karin bayani.