A kokarin magance kalubalen tsaro dake addabar jihar Zamafara, gwamnatin jihar ta ce a rufe dukkanin wasu kasuwannin dabbobi a jihar.
Hakan ya biyo bayan korafe korafen da ake na cewa ana yawan kai dabbobin sata a irin wadannan kasuwanni.
To amma meyasa aka maida hankali a kasuwannin dabbobi kadai? abin da shirin mu na Najeriya a yau ya maida hankali kenan.