Hukumar kula da Kafofin Yaaɗa Labarai ta Najeriya (NBC) na shirin ɓullo da wasu matakai kan masu amfani da shafukan sada zumunta na zamani a wani yunkuri na tsaftace ɓangaren domin hana gurbata tarbiyyar ’yan kasar nan.
Anya zai yi wu a sanya ido yadda ya kamata a kan kafofin sada zumunta yadda ya kamata a Najeriya?
An sha kai ruwa rana da ’yan Najeriya kan wannan kuduri na gwamnati, a shirin Najeriya A Yau mun duba hanyoyi da irin waɗannan matakai za su yi aiki ba tare da matsala ba.