Rahotanni daga wadansu jihohin Najeriya na bayyana cewa an samu karuwan adadin yara kanana da ke shekarun zuwa makaranta a matsayin mabarata a kan titunan da lungunan manyan unguwanni a sassan kasar nan.
Shin mene ne ya kawo wannan lamari na adadin yaran da ke bara a tsakanin jamaá a daidai wannan lokaci da ake kurin cigaba, wayewa da sanin kimar bil-Adama?
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya dubi wannan batu, ya leka jihar Legas, Kano da kuma jihar Filato da ke arewa ta tsakiyar Najeriya.