’Yan Najeriya mazauna yankunan da ke iyakar kasar Jamhuriyar Nijar na dandana kudarsu sakamakon tsadar rayuwa da tashin gwauron zabon kayan masarufi, tun bayan rufe bodar da Najeriya ta yi a watan Agusta.
Anya wannan rufe boda da Kungiyar ECOWAS ta sa aka yi, ba za a ci kai da kai ba?
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya ziyarci garin Illela a Jihar Sakkwato da Maigatari a Jihar Jigawa, da kuma Kwangalam da Jibiya a Jihar Katsina, domin jin halin da mazauna garuruwan suka tsinci kansu a tsawon lokacin da ka rufe bodar, a matsayin garuruwan ma masu alakar kasuwanci da makwabtansu da ke Nijar.
Shirin na kuma dauke da fashin baki tare da wani masanin tattalin arziki a game da wannan al’amari.