Abin Da Ya Sa Iyaye Ke Tsoron Malamai Su Hukunta ‘Ya’Yansu

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Abin Da Ya Sa Iyaye Ke Tsoron Malamai Su Hukunta ‘Ya’Yansu
Oct 23, 2023
Muhammad Auwal Sulaiman, Muslim Muhammad Yusuf, Nana Khadija Ibrahim

Send us a text

A Shekarun baya iyaye kan damka amanar ‘ya’yansu kacokan ga malamai domin karatu da tarbiyya, wannan kuma ba iya malaman addini kadai ba, harda malaman makarantun  boko. 

Sai dai a ‘yan shekarun nan, iyaye sun samu shakku dangane da hukunta ‘ya’yansu a makaranta, mene ne abin da ya janza har aka samu kai a irin wannan hali? 

Shirin Najeriya A Yau na tafe da tattaunawa ta musamman da kwararrun malaman makarnata, masu makaranta da kuma iyayen yaran.