Ana murna da raguwar hare-haren 'yan ta'adda a yankin Arewa maso gabas, sai ga shi wasu alamu na nuna akwai yiwuwar wasu na shirin dawo da hannun agogo baya.
A 'yan kwanakin nan an samu barazanar kai hare-hare da wasu bayanan sirri a yankunan da ake ganin an ci ƙarfin 'yan ta'addan.
Shirin Najeriya a Yau ya duba yadda 'yan ta'adda ke yunƙurin dawo da kai hare-hare a yankin arewa maso gabashin Najeriya.