Sayen kuri’a daya ne daga cikin abubbuwan da masana ke bayyanawa a matsayin wani abu da ke tadiye kafar Dimukuradiyya a Najeriya.
Mene ne abin da ya kamata a yi domin hana sayen kuri’a?
Shirin Najeriya A Yau ya dubi yadda ake sayen kuri’a a zabukan Najeriya, ya kuma tattauna da masana kan hanyoyin da za a bi domin magance wannan matsala.