Shin Ko Akwai Lalaci Kan Yadda Wasu Mazan Kan Sakarwa Matan Su Ragamar Gida
Najeriya a Yau
More Info
Najeriya a Yau
Shin Ko Akwai Lalaci Kan Yadda Wasu Mazan Kan Sakarwa Matan Su Ragamar Gida
Nov 24, 2023
Muhammad Auwal Sulaiman, Muslim Muhammad Yusuf, Nana Khadija Ibrahim

Tun dauri a arewacin Naijeriya, Maza aka sani da rike da ragamar gida, ta hanyar fita a nemo abun da za a ciyar da iyali, yayin da mata ke lura da aikace-aikacen gida.

Wasu matan kan yi sana’o’i na gida da niyyar samun kudin kashewa da ba dole sai an tambayi maigida ba.

To a yanzu an shiga yanayin da wasu mazan ke sakarwa mata ragamar gida kacokan. 

Shirin Naijeriya A Yau, ya yi duba ne kan wannan ta’ada ta wasu mazajen, da yadda matan ke fama wajen daukar nauyin gida.