Ana ta kai ruwa rana a majalisar jihar Filato gameda yadda shugabanci zai kasance daga ɗan jam'iyar adawa da ba su da rinjaye.
Akwai 'yan majalisar APC da kotu ta baiwa nasara bayan tsige mafi yawancin yan jam'iyar PDP, duk da yake ba a rantsar da su ba amma majalisa tana hutu.
Shirin Najeriya a Yau ya duba yadda ake tirka-tirka a majalisar dokokin jihar Filato da zargin barazanar tsige kakakinta.