Makomar Ministar Jinkai Betta Edu Da Shugabar NSIP Halima Shehu

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Makomar Ministar Jinkai Betta Edu Da Shugabar NSIP Halima Shehu
Jan 09, 2024
Muhammad Auwal Sulaiman, Muslim Muhammad Yusuf, Nana Khadija Ibrahim

Send us Fan Mail

Tun bayan dakatar da ministar jin kai ta Najeriya Betta Edu a jiya Litinin 8 ga Janairu da kuma Halima Shehu daga matsayin  shugabar hukumar bada tallafin dogaro da kai ta kasa kwanaki 6 tsakani 'yan Najeriya sun fara bin kwakkwafin wane hali su ke ciki, kuma mene ne abin da ya sa aka dakatar da su? 

Shirin Najeriya A Yau ya binciko cikakken abin da ake zarginsu, ya kuma ji ta bakin masanin shari'a kan makomar wanda ya aikata abin da ake zarginsu da shi.