Jihohin Kano da Filato na hannun jam'iyyun adawa a matakin ƙasa. Tun bayan hukuncin kotun ƙoli ana ta hasashen ya makomarsu za ta kasance.
Akwai yiwuwar su iya saita alƙiblar gwamnati idan sun yi adawa mai ma'ana, yayinda ake sa ran gwamnati ta tafi da kowa.
Shirin Najeriya a Yau ya duba halin da 'yan adawa ke ciki a waɗannan jihohi.