Abin Da Ya Sa Gwamnonin Arewa Suka Je Amurka Taron Tsaro

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Abin Da Ya Sa Gwamnonin Arewa Suka Je Amurka Taron Tsaro
Apr 29, 2024
Muhammad Auwal Sulaiman, Muslim Muhammad Yusuf, Nana Khadija Ibrahim

Send us Fan Mail

Gwamnonin Arewacin Najeriya da ake fuskantar kalubalen tsaro na kokarin lalubo ko ta wace hanya a samu dabarar dakile matsalar.

Tafiyar  gwamnoni 9 daga arewacin Najeriya zuwa Amurka a kwanan nan domin halartar taron tsaro ya nuna yadda suke kokarin daidaita lamarin har a matakin kasashen ketare.

Saidai lamarin na zuwa ne a lokacin da wasu ke ganin an yi makamancinsa a Najeriya ba tare da halartar wani gwamna daga jihohin da suke fama da matsalar tsaron ba.

Shirin Najeriya a Yau ya duba tasirin da taron zai yi wajen magance matsalar yankunan.