Dalilan Da Ake Yi Wa Mutum Kutse A Soshiyal Midiya

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Dalilan Da Ake Yi Wa Mutum Kutse A Soshiyal Midiya
May 03, 2024
Muhammad Auwal Sulaiman, Muslim Muhammad Yusuf, Nana Khadija Ibrahim

Send us Fan Mail

Masu amfani da shafukan sada zumunta kan fada hannun masu dandantsa inda sukan yi kutse a shafin mutum har ya rasa iko da shi.

Kwararru sun ce ana yi wa wasu hakan domin bata suna ko kuma neman kudi da damfara.

Shirin Najeriya a Yau ya tattauna da kwararru a fannin samar da matakan tsaro a soshiyal midiya game da dabarun inganta tsaron shafukanku.