Yadda Ambaliya Ke Raba Dubban ‘Yan Najeriya Da Muhallansu

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Ambaliya Ke Raba Dubban ‘Yan Najeriya Da Muhallansu
Aug 29, 2024
Suleiman Hassan Jos, Idris Daiyab Bature

Send us Fan Mail

Wata Babbar matsala da ambaliyar ruwa ke haifarwa a Najeriya ita ce, yadda dubban mutane ke rasa muhallansu a duk shekara.

Alkalumman hukumar bayar da Agajin gaggawa ta NEMA sun nuna cewa kawo yanzu, ambaliyar ta raba kusan mutum dubu 208,655 da muhallansu a jihohi 28.

Shirin Najeriya a Yau, ya tattauna kan irin matakan da suka kamata a dauka domin kaucewa matsalar da hakan ka iya haifarwa ga al'umma.