Shin Dole Ne Sai An Dauki Tsauraran Matakan Saita Najeriya?

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Shin Dole Ne Sai An Dauki Tsauraran Matakan Saita Najeriya?
Sep 12, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us Fan Mail

Duk da kokawa da Yan Najeriya ke ci gaba da yi kan irin manufofin gwamnati da suka ce suna Kara jefa su cikin kangin rayuwa.

Amma, a ko da yaushe Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu Yana kara nanata cewa, tilas ne a dauki tsauraran Matakai na saita tattalin arzikin kasar, idan har ana bukatar Jin dadi a nan gaba.

Shirin Najeriya a Yau zai tattauna ne, kan ko tilas ne sai an dauki tsauraran Matakan, kafin saita tattalin arzikin Najeriya?