Kudurorin Dokar Haraji da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya aike wa Majalisar Dokoki ta Kasa suna ci gaba da tayar da kura a Najeriya.
Muhawara a kan batun ta dauki sabon salo ne bayan da wasu malaman addinin Musulunci daga Arewacin Najeriya suka ki amincewa da wasu tanade-tanaden kudurorin dokar.
Shin har da kaza ne a cin danko? Karambani ne ya sa malamai tsoma baki a muhawarar ko neman maslaha ga al’umma?
A kan wadannan batutuwa shirin Najeriya A Yau zai yi nazari.