‘Karambanin’ Malamai Kan Ƙudurorin Harajin Tinubu

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
‘Karambanin’ Malamai Kan Ƙudurorin Harajin Tinubu
Dec 05, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us Fan Mail

Kudurorin Dokar Haraji da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya aike wa Majalisar Dokoki ta Kasa suna ci gaba da tayar da kura a Najeriya.

Muhawara a kan batun ta dauki sabon salo ne bayan da wasu malaman addinin Musulunci daga Arewacin Najeriya suka ki amincewa da wasu tanade-tanaden kudurorin dokar.

Shin har da kaza ne a cin danko? Karambani ne ya sa malamai tsoma baki a muhawarar ko neman maslaha ga al’umma?
A kan wadannan batutuwa shirin Najeriya A Yau zai yi nazari.