Dalilan 'rashin yanke' wa masu laifi hukunci a Najeriya

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Dalilan 'rashin yanke' wa masu laifi hukunci a Najeriya
Dec 20, 2021
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

’Yan Najeriya da dama na mamakin yadda mutanen da suke gani a matsayin manyan masu laifi ke kubuta idan an kai su gaban kotu.

Sau tari ana murnar an kama mai laifi, amma ana zuwa kotu sai yanke hukunci ya gagara a cikin lokaci; Wani lokaci kuma bayan dan lokaci da yanke mishi hukunci, sai a ga ya dawo cikin al’umma yana harkokinsa.

Ina gizo ke saka, sannan me ya sa mutane debe kauna daga cin nasara a kotunan Najeriya?