Yadda Rage Kwanakin Zuwa Makaranta Zai Shafi Dalibai A Jihar Kaduna

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Rage Kwanakin Zuwa Makaranta Zai Shafi Dalibai A Jihar Kaduna
Jan 11, 2022
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed

Send us a text

Bayanin rage adadin kwanakin zuwa makaranta da Gwamnatin Jihar Kaduna ta fitar a wannan zango ya dauki hankalin malaman makarantu da masana harkar ilimi a Jihar. 

Malaman Makaranta na ganin cewa tsarin da zai tilastawa makarantu hutun kwana 3 a sati  zai kara takure su wurin shirya jadawalin darussan da za su koyar.

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci na kunshe da tattaunawa ta musamman da Malamai da masana harkokin ilimi akan wannan batu.