A kwana akalla 220 da gwamnatin Nejeriya ta rufe harkokin kafar sada zumunta ta Twitter, ‘yan kasar sun tafka asarar makudan kudade, a yayin da gwamantin kasar kuma ta ci gagarumar riba a sakamakon matakin da ta dauka.
Masana sun yi bayanin irin makudan kudaden da Gwamnatin Tarayya za ta rika samu daga harajin da za ta rika karba daga hannun kamfanin Twitter a sakamakon amfanin da ’yan Najeriya suke yi da kafarsa, wurin gudanar da harokinsu na kasuwanci da kuma sadar da zumunta.