Fashewar Tankar Mai: Asarar Da Al’ummar Majiya Suka Tafka

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Fashewar Tankar Mai: Asarar Da Al’ummar Majiya Suka Tafka
Oct 18, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us Fan Mail

Galibin waɗanda suka rasa rayukansu sakamakon fashewar tankar man da ta yi ajalin sama da mutum 150 a garin Majiya na Jihar Jigawa matasa ne.

Ɗaya daga cikinsu, Hassan Hamza, matashi ne da ya yi karatu a fannin Harhaɗa Magunguna, karatun da ake matuƙar buƙatar masu yinsa a tsakanin al’umma.

A shirin Najeriya a Yau na lokacin za mu yi nazari ne a kan girman asarar da al'ummar Jami’ar Jihar Jigawa ta tafka.