Al’ummar Majiya a Jihar Jigawa na ci gaba da jimamin mutuwar mutum sama da dari sakamakon hadarin tankar mai.
Saboda tashin hankalin da suke ciki, wasu daga cikin mazauna garin sun ma ce sun kasa cin abinci.
Shirin Najeriya a Yau zai tattauna da wasu daga cikin ’yan uwan wadanda abin ya shafa game da yadda suka ji da faruwar wannan lamari.