Shirin Da Masu Ruwa Da Tsaki Suka Yi Kan Zaben Ondo.

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Shirin Da Masu Ruwa Da Tsaki Suka Yi Kan Zaben Ondo.
Nov 15, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us a text

A ranar Asabar 16 ga wannan watan ne za’a gudanar da zaben gwamna a jihar Ondo, sai dai kamar sauran zabukan da aka saba gudanarwa a Najeriya, tuni masu ruwa da tsaki suka bayyana kammala shirye shiryen tunkarar wannan zabe.

To amma ba’a nan gizo ke sakar ba, domin kuwa a mafi yawan lokuta al’umma a kasar nan na korafin cewar duk da shirye shiryen da masu ruwa da tsaki suke bayyana kammalawa, a karshe ana samun matsala.

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai tattauna da masu ruwa da tsaki ne kan yanayin shirye shirye don tunkarar zaben gwamna a jihar Ondo.