Matakan Da Manoman Jihar Taraba Suka Dauka Kan 'Yan Ta'adda

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Matakan Da Manoman Jihar Taraba Suka Dauka Kan 'Yan Ta'adda
Nov 28, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us a text

Wata matsala da kasar nan ke cigaba da fuskanta itace matsalar karancin abinci sakamakon ‘yan ta’adda dake barnata amfanin noma, hana manoma yin noma, a wasu lokutan ma karbar kudaden haraji daga manoma a wasu yankunan kasar nan.

Hakan yasa alummomin Karamar hukumar Gassol da Balli dake jihar Taraba daukar wasu matakai don samawa kan su mafita daga ayyukan irin wadannan yan ta’adda.

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai tattauna ne kan irin matakan da alummar wadannan yankuna suka dauka don gudanar da ayyukan noma.