Yankin karamar hukumar Birnin Gwari dake jihar Kaduna na daya daga cikin alummomin da suka fi fuskantar matsalar tsaro musamman a arewacin Najeriya.
A kwanan nan rahotanni sun bayyana cewa gwamnatin jihar ta shiga yarjejeniya tsakanin yan bindigan da kuma gwamnatin jihar.
Shirin Najeriya A Yau yayi Nazari ne kan wannan yarjejeniya da kuma abun da hakan ke nufi ga jihar da ma alummar yankin.