Sashe na 4 na kundin tsarin mulkin kasa na dauke da tanadetanade musamman da suka shafi ‘yancin dan adam a dokar Najeriya.
Cikin tanade-tanaden akwai ’yancin da doka ta bai wa kowane dan najeriya na rayuwa, da shiga taro, da fadin albarkacin baki.
Shirin Najeriya A Yau zai yi duba a kan tanade-tanaden doka a kan ’yancin fadin albarkacin baki.