Kuncin Da Marasa Lafiya Suke Ciki Sakamakon Tsadar Magani

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Kuncin Da Marasa Lafiya Suke Ciki Sakamakon Tsadar Magani
Dec 09, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us a text

Farshin maganin asibiti yana ci gaba da tashin gwauron zabo a Najeriya, inda yake jefa marasa lafiya da ’yan uwa da abokan arziki cikin halin tsaka mai wuya.

Da yawa daga cikin marasa lafiya dai sukan koma amfani da abin da ya fi musu sauki – ko dai sayen maganin a hannun masu tallansa a kafada, ko amfani da maganin gargajiya, ko kuma, a wasu lokutan, hakura da maganin.

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan halin da marasa lafiya sukan shia sakamakon tashin gwauron zabo da maganin asibiti ya yi.