Yadda Matsalar Cin Zarafin Mata Ta Zama Karfen Kafa A Najeriya

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Matsalar Cin Zarafin Mata Ta Zama Karfen Kafa A Najeriya
Dec 10, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us a text

Cin zarafin mata a Najeriya matsala ce da ke ci gaba da ci wa masu ruwa da tsaki a Najeriya kwarya.

Hanyoyin cin zarafin na mata dai suna da yawa; kama daga lakada musu duka zuwa yi musu fyade da wasu abubuwan da dama.

Ko wanne irin hali mata suke shiga sakamakon cin zarafi a gidajen aurensu?
Shirin Najeriya a Yau zai yi magana da matan da aka ci zarafinsu da ma mazan da suka ci zarafin matansu don gano bakin zaren.