Yadda Tamowa Ke Yaduwa Kamar Wutar Daji a Katsina

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Tamowa Ke Yaduwa Kamar Wutar Daji a Katsina
Dec 17, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us Fan Mail

Wani rahoto da Kungiyar Likitoci ta Médecins Sans Frontières (MSF) ta fitar ya nuna cewa Arewa maso Yamma ta fi kowacce shiyya yawan karuwar yara masu tamowa.

A shiyyar kuma, inji rahoton, Katsina ta fi ko wacce jiha yawan masu fama da cutar.

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi bincike ne don gano yadda lamarin yake.