Yadda ’Yan Najeriya Suka Jure Wa Matsin 2024

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda ’Yan Najeriya Suka Jure Wa Matsin 2024
Dec 30, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us Fan Mail

Tun bayan rantsar da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a watan Mayun bara ne dai ’yan Najeriya suke ta kokawa da matsin tattalin arziki sakamakon wasu tsare-tsare da manufofi da Gwamnatin Tarayya ta bijiro da su.

Wadannan manufofi sun hada da janye tallafin man fetur da kyale kasuwa ta yi halinta a kan darajar Naira da janye tallafin wutar lantarki da sauran su.

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci za iyi tsokaci ne a kan jimirin da ’yan Najeriya suka yi a shekarar.