Amfanin Komawa Makaranta A Ranar Da Aka Bude Bayan Hutu

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Amfanin Komawa Makaranta A Ranar Da Aka Bude Bayan Hutu
Jan 07, 2025
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us Fan Mail

Malamai na dauri sun karantar da cewa idan mutum ya bar karatu na kwana daya, karatun zai bar shi tsawon mako guda; idan ya bar karatu mako guda, karatun zai bar shi wata guda.

Sai dai a yau, a duk lokacin da aka ce an koma makaranta bayan hutu, a kan samu rashin komawar dalibai a ranar da aka koma – a wasu lokutan ma, har da malamai.

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari tare da bayar da shawarwari ne a kan amfanin komawar dalibai makaranta a ranar da aka bude ta.