A wannan zamani, ’yan Najeriya da dama ba sa samun wadataccen abinci a yini.
Magidanta da dama, musamman, sun tsallake sun bar iyalansu sun shiga bariki don neman na sanyawa a bakin salati.
Mene ne dalilin hakan, kuma yaya za a yi a kauce wa fadawa cikin irin wannan yanayi?
Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan halin da galibin ’yan Najeriya suka tsinci kansu a ciki na rashin samun abinci yadda ya kamata