Yadda Kuɗin Kujera Yake Neman Hana Maniyyata Sauke Farali

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau
Yadda Kuɗin Kujera Yake Neman Hana Maniyyata Sauke Farali
Jan 21, 2025
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us a text

Yanzu haka, saura mako biyu wa’adin  da aka deba wa maniyyata Hajjin bana su biya kudin kujerar ya cika, amma rahotanni daga wasu sassan kasar nan na nuna cewa kalilan ne suka iya biyan.

Kudin kujerar hajjin ya tsorata ’yan Najeriya a bana, bayan da hukumomi suka ce duk mai sha’awar sauke farali sai ya biya zunzuruntun kudi sama da Naira miliyan takwas.

Wannan shine batun da shirin Najeriya  A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.